*πŸ’ŸπŸ’Ÿ UWA KO ÝAπŸ’ŸπŸ’Ÿ*

*written by:*
*FAREEDAH GURKUπŸ’š*



*Edited by:ANEELURV😍*



*Dedicated to my lovely mom😍*



*pg 17▶18*



"Feenerh",
Muryar mommy taji tana kiranta,
"Naam mommy gani nan zuwa",
Tafito ta sameta a falo,
"Mommy gani",
"Yawwa dama ni fita zanyi",
"Ina zaki tafi mommy",
"Kinsan kawata salamatu bata da lafiya ,so zanje in duba ta ne",
"Okay mommy ,allah ya kara mata lafiya",
"Ameen ,nina wuce",
Feenerh na shirin komawa daki kenan sai sallanar khadija ya tsayar da ita ,bayan sun gama gaisuwa da mommy sai ta shigo falo ta sameta.
"Feenerh ko kema angwan zaki",
"A'a",
"Okay, so kawata yakike",
"Lafiya kalau kawata, kwana biyu baki shigo bako",
"Things ne sukamin yawa, ranan ma umma tace min kinzoko bana nan"
"Eh hakane, dama i was passing by shine nace bari in dubaki sai kuma akacemin ba kya nan",
"Wallah kam rannan bana gida",
"Toh kawata mushiga ciki",
Suka shiga daki,feenerh ta dauko mata lemon kwali mai sanyi tabata,sannan ta debo mata snacks ta hada mata dashi.
"Feenerh",
"Naam",
"Meya faru ne duk kin rame",
"Ramewa kuma ,mesa kikace haka",
"Saboda duk fuskarki ya koma ciki,meke damunki",
"Nidai ba abinda ke damuna banason sharri khadija",
"I hope dai ba tafiyar musa ce tasa kika rame ba",
"Toh in kika danganta ramewa na da tafiyarsa ,kinyi daidai saboda gaskiya khadija am missing him like crazy",
"Hmmm feenerh kenan , nasan haka za'a aikata,amma yanzu musa ya kiraki da sabuwar lambarsa ta can",
"Eh ya kirani jiya da daddare",
"Okay toh ,inaga sabanin lokaci ne akasamu",
"Eh hakane ne ,amma yace yau in sha allahu zai kira ni",
"Lallai na tabbata shima missing  Δinki yake sosai",
"Allah ko kawata",
"Ofcurse ,saboda kwatakwata yaushe ya tafi kuma gashi har ya sayi sabon layi ya kiraki",
"Hakane kjadija ,yama cemin akan da numbata ya fara launching sim  Δinsa",
Kingani koh".
"Khadija",
"Naam",
"Yau daddy na yakirani yana min magana akan wancan zancen fa",
"Toh kice lallai iyayenki da gaske suke ",
"Wallahi fa",
"Toh tunda already kina da mijin aure ai shikenan",
"Yawwa feenerh ,ja'afar zai dawo next week",
"Kice allah kawata",
"Wallahi",
"Yanzu shikenan ya gama degree dinsa ",
"Eh",
"Lallai ba wuya",
"Haka fa,so kidaina wannan tunani tunaniki saboda banaso ya gane kamar wani abu na damunki ,kinsan yadda yake"
"Nafa sani, yanzu zai fara bincike",
"Wallahi fa,kamar wani CID",
"Toh allah ya dawo dashi lafiya,munyi missing  Δinshi",
"Nidai banyi missing  Δinshi ba"khadija tace,
"Ba wanda ya kaiki missing  Δinshi, nasan allah allah kike ya dawo",
"Oho dai".
Ahaka suka cigaba da hira har yamma sannan sukayi sallama khadija ta koma gida.
Har yanzu musa bai kira taba kuma gashi karfe biyar na yamma yayi. Yace mata da safe zai kirata, toh har yanzu meya ke jira sai ta tuna au ai lokacin mu ba daya bane.



*tnx for reading....*
*©Fareedah*

Comments

Popular Posts